1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Iran ta yi tir da hari a ofishin jakadancin Saudiya

Lateefa Mustapha Ja'afarJanuary 20, 2016

Jagoran addinin Islama na kasar Iran Ayatollah Ali Khamenei ya yi tir da harin da wasu da suka fusata suka kai a ofishin jakadancin Saudiya da ke Tehran babban birnin kasar.

https://p.dw.com/p/1Hh9f
Jagoran addinin Islama na Iran Ayatollah Seyed Ali Khamenei
Jagoran addinin Islama na Iran Ayatollah Seyed Ali KhameneiHoto: Leader.ir

Khamenei ya bayyana harin da cewa ya tozarta kasarsa da ma addinin Musulunci. Khamenei wanda ya bayyana haka a shafinsa na Internet, ya kuma yabawa dakarun juyin-juya hali na kasar dangane da tsare mayakan ruwa na Amirka na wani dan lokaci da suka yi a makon da ya gabata, sakamakon keta kan iyakar ruwan kasar ta Iran da suka yi. A ranar biyu ga wannan wata na Janairu da muke ciki ne dai wasu masu zanga-zanga domin nuna fushinsu dangane da zartas da hukuncin kisa a kan shahararren malamin addinin Islamar nan mabiyin mazhabar Shi'a dan asalin kasar ta Saudiya, Ayatollah Nimr Baqir Nimr da mahukuntan Saudiyan suka yi, suka kai hari a kan ofishin jakadanicn Saudiyan da ke Tehran babban birnin kasar ta Iran inda suka cinna masa wuta.