1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Kokarin neman mafita a Najeriya

September 28, 2017

A Najeriyar sassa daban-daban na masu ruwa da tsaki sun kaddamar da tattaunawa a tsakanin manya da kabilu na kasar da nufin  neman mafita ga makomar kasar.

https://p.dw.com/p/2ktuN
Mataimakin shugaban Najeriya da wakilan majalisar ministoci na kasa
Mataimakin shugaban Najeriya da wakilan majalisar ministoci na kasaHoto: Novo Isioro

Har ya zuwa yanzun dai babbar matsala a tsakanin 'yan mulki dama talakawa a Najeriyar dai na zaman amsa tambaya muhuimmiya guda game da gamsuwa da yadda tsarin kasar ke tafiya a lokaci mai nisa. Duk da cewar dai an doshi shekaru har 60 ana faduwa ana sake tashi, hankoro na kuma kara karuwa tsakanin masu neman da a ware da masu tunanin sake tsarin da muryarsu ke kara karfi cikin kasar a halin yanzu.

Manyan 'yan boko da 'yan siyasar na Najeriya sun hadu suka yi tunanin cewar akwai bukatar a samu mafita ga halin da kasar take cki a karkashin jagorancin tsohon shugaban kasar Najeriya General Yakubu Gowon. Farfesa Jerry Gana dai na zaman daya a cikin wakilai daga yankin arewa ta tsakiya a cikin  wata tattaunawa da kungiyar tattaunawa da ci gaba mai zaman kan ta da ke a Abuja ta kai ga shiryawa da nufin nazarin bukatu na 'yan kasar sannan kuma da neman hanyar dorawa cikin kokarin ginin kasar da ke neman rushewa.