Kira ga soma aikin hadin kai a Libiya
October 19, 2015Kasashen duniya da dama sun yi kira a wannan litanin ga bangarorin da ke gaba da juna a kasar libiya da su gaggauta sanya hannu kan yarjejeniyar kafa gwamnatin hadin kan 'yan kasa da suka cimma a karkashin jagorancin Majalisar Dinkin Duniya .
Kasashen da suka hada da Amirka da Tarayyar Turai da na Larabawa sun sanya wannan kira ne a cikin wata sanarwar hadin guywa da suka fitar a wannan Litinin a birnin Paris inda suka ce a shirye suke su kawo goyon bayansu ga gwamnatin hadin kan kasar Libiyar dama kawo mata dauki a fannin yaki da ayyukan ta'addanci.
Ranar tara ga wannan wata na Oktoba ne bangarorin da ke gaba da juna a kasar ta Libiya suka cimma matsaya kan sabuwar gwamnatin hadin kan kasar mai kunshe da mambobi 17 a karkashin jagorancin Firaminista Fayez el-Sarraj. Sai dai har kawo yanzu babu bangaren da ya saka hannunsa a kan yarjejeniyar a hakumance.