1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaAfirka

Kenya da Amurka na son a rage wa Afirka nauyin basuka

May 23, 2024

Shugabannin kasashen Kenya da na Amurka za su bukaci manyan kasashe masu karfin arziki da su dubi yiwuwar rage wa kasashe masu tasowa nauyin basukan da ke nakasa a halin da ake ciki.

https://p.dw.com/p/4gCyw
Shugaba Joe Biden da William Ruto na Kenya
Shugaba Joe Biden da William RutoHoto: Susan Walsh/AP Photo/picture alliance

Yayin ziyarar kwanaki uku ta aiki da shugaban Kenya William Ruto ke yi a Amurka ne dai ya zanta da Shugaba Joe Biden a game da wannan bukata.

Wannan shi ne karo na farko cikin sama da shekaru 15 da ake samun wani shugaba na Afirka ke ziyara makamancin wannan a hukumance a birnin Washington.

Shugabannin biyu sun kuma ce suna shirye nan ba da jimawa ba, da su bayyana wata sabuwar taswiarar samar da ci gaba tsakanin kasashen Kenya da Amurka da suka yi wa lakabi da Nairobi-Washington Vision.

Tuni ma dai Amurka ta bayyana ware dala miliyan 250 da za a yi amfani da su wajen taimaka wa kasashe matalauta dake fama da radadin tattalin arziki.