1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Kebbi: Wata ta kubuta cikin daliban da aka sace

November 18, 2025

Daya daga cikin 'yan mata dalibbai 25 da aka yi garkuwa da su a jihar Kebbi da ke arewa maso yammacin Najeriya ta samu kubuta ta koma gida

https://p.dw.com/p/53pyX
Takalman daliban da aka yan bindiga suka sace
Takalman daliban da aka yan bindiga suka saceHoto: KOLA SULAIMON/AFP

An sace dalibban mata ne a lokacin da wasu 'yan bindiga suka kai hari a wata makarantar Sakandaren 'yan mata da safiyar litanin ta wannan mako da misalin karfe 4, inda suka yi awon gaba da wadannan 'yan mata 25, kana suka kashe mataimakin shugaban makarantar da wani maigadi.

Dalibar da ta gudo daga cikin daji 'yan sa'o'i bayan satar a makarantar Government Girls Comprehensive Secondary School, in ji Musa Rabi Magaji, shugaban makarantar.

Sace-sacen dalibbai ya zama ruwan dare a arewacin Najeriya inda kungiyoyin 'yan bindiga da masu ikirarin jihadi suke gudanar da wannan aiki, Kuma galibi makarantu ne 'yan bindigar suka fi mayar da hanakali kamar yadda masana ke cewa.

Kawo yanzu dai ba bu wata kungiya da ta dauki alhakin wannan aika-aika.

Ko a shekarar 2021 wasu 'yan bindiga sun sace dalibbai mata a makaranatar mata a karamar hukumar Yawuri ta jihar Kebbi.

Masu sharhi na zargin cewa karuwar cin hanci da rashawa ya kawo nakasu ga samar da wadataccen makamai ga Jami'an tsaro abin da ake zargin ya haifar da karuwar hare-hare.