1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Tsauraran matakan tsaro gabanin gangami a Kashmir

Zainab Mohammed Abubakar
August 23, 2019

Hukumomin Indiya sun tsaurara matakan tsaro a Lardin Kashmir, biyo bayan kiran da 'yan awaren suka yi na gudanar da gangamin adawa zuwa ofishin MDD, gabanin sallar Juma'a.

https://p.dw.com/p/3OMAj
Pakistan Kaschmir Protest & Unruhen in Lahore
Hoto: Reuters/M. Raza

Kawo yanzu dai mutane 152 ne suka jikkata daga hayaki mai sanya hawaye a Lardin Kashmir mai fama da rikici, tun bayan da jami'an tsaron Indiya suka kaddamar da somame a watan da ya gabata.

Hukumomin Indiyan sun aike da karin rundunar tsaro, tare da haramta wani gangami na al'umma, daura da yanke hanyoyin sadarwa ta wayar salula da ma yanar gizo, a wani mataki na kare aukuwar zanga zanga mai karfi, tun bayan sanar da janye matsayin 'yancin da lardin ke da shi a ranar biyar ga watan Augusta.

Sai dai duk da wadannan matakai, jama'a musamman matasa kan yi jerin gwano a kan titunan babban birnin Lardin watau Srinagar, musamman a ranakku kamar Juma'a su na jifa da duwatsu, matakin da ya janyo martani daga jami'an tsaro.