1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Karancin sabbin kudi ya haifar da zanga-zanga a Najeriya

Binta Aliyu Zurmi
February 8, 2023

Rahotanni daga Najeriya na cewar wasu masu zanga-zanga a birnin Abeokuta da ke jihar Ogun a kudancin kasar sun kai hari a wasu manyan bankuna tare da kona tayoyi a kan tituna.

https://p.dw.com/p/4NDU5
Nigeria Unruhen Wahlen Jugendliche
Hoto: picture-alliance/dpa

Rashin sabbin kudi da al'umma ke fuskanta tun bayan da aka sake fasalta wasu takardun naira a kasar da ke ci gaba da janyo dogayen layi a bankuna ya fusata masu boren.

Mai magana da yawun 'yan sandan jihar ta Ogun Abimbola Oyeyemi ya shaidawa kamfanin dillancin labarai na AFP cewar zanga-zangar ta barke a wasu garuruwa 3 na jihar, inda masu boren suka farfasa wasu bankuna biyu tare da kona tayoyi a kan tituna.

Wannan na zuwa ne kasa da makwanni uku kafin al'ummar kasar su garzaya rumfunan zabe, Najeriya kasar da ta fi yawan al'umma a nahiyar Afirka na fuskantar karancin sabbin kudin a yayin da aka daina karbar tsofafin, kazalika ana fuskantar karancin man fetur, 
 
Ko a makon da ya gabata an gudanar da bore a wasu manyan garuruwan kasar.