Janar Musa zai maye gurbin Badaru a ma'aikatar tsaro
December 2, 2025
Shugaban Bola Ahmad Tinubu ya nada Janar Christopher Gwabin Musa a matsayin sabon ministan tsaro na kasa. A cikin wata wasikar da ya aike wa shugaban majalisar dattawa, Godswill Akpabio, Shugaba Tinubu ya bayyana cewa Janar Musa zai maye gurbin Alhaji Mohammed Badaru Abubakar, wanda ya yi murabus bisa dalilai na rashin lafiya.
Janar Musa gogaggen soja a ma'aikatar tsaron Najeriya
Janar Musa, wanda zai cika shekara 58 a ranar 25 ga Disamban 2025, fitaccen soja ne da ya jagoranci rundunar tsaron Najeriya a tsakanin shekarar 2023 zuwa Oktoba 2025. Ya kuma taba lashe lambar yabo ta Colin Powell Award for Soldiering a shekara ta 2012.
Ta'asar 'yan bindiga na satar dalibai a Najeriya
An haifi Janar Musa a jihar Sokoto a 1967, kuma ya yi makarantar firamare da sakandare a jihar, kafin ya tafi College of Advanced Studies a Zariya. Ya kammala a 1986, sannan ya shiga ma'aikatar horon aikin soja ta Nigerian Defence Academy, inda ya samu digirin farko a 1991.
Shugaba Tinubu na da kyakyawan fata ga Janar Christopher
A 2019, Janar Musa ya jagoranci sashe na uku na runduna ta musamman ta "Operation Lafiya Dole", tare da jagorantar sashe na uku na rundunar tsaro ta hadin gwiwa da ke yaki da Boko Haram a yankin Tafkin Chadi.
A cikin wasikarsa, Shugaba Tinubu ya bayyana cikakken kwarin gwiwa cewa Janar Musa zai kara inganta tsaron Najeriya tare da jagorantar ma’aikatar tsaron kasar kamar yadda ya kamata.