MDD ta ce ISWAP ta sako jami'an hukumar
June 16, 2021Talla
An dai kai ga nasarar sakin mutanen ne bayan kwashe tsawon makwannin ana tattaunawa da masu yin garkuwar. Daga cikin wadanda aka sako har' da wani jami'in hukumar abinci ta Majalisar Dinkin Duniya PAM da na kungiyar agaji ta Red Cross da kuma wani ma'aikacin hukumar 'yan gudun hjirA ta MDD wadanda aka sace tun cikin watan Disamba da ya gabata a Maiduguri.