Iran ta kama masu leken asiri 30
March 10, 2026
Talla
Ma'aikatar tattara bayanan sirri ta Iran ta ce tana cigaba da tsare mutanen da ta kama a mastayin masu leken asiri na cikin gida da wasu jami'an kasashen Isra'ila da Amurka.
Kamen na zuwa ne a daidai lokacin da ake ci gaba da samun tashe-tashen hankula a yankin Gabas ta Tsakiya, Iran ta sha zargin Isra'ila da hukumomin leken asiri na yammacin duniya a matsayin zagon kasa a cikin kasar, musamman a kan sojojinta da makaman nukiliya. Jami'an Isra'ila ba kasafai suke yin tsokaci kan irin wannan zargi ba.