Hizbullah ta yi watsi da yarjejeniyar Isra'ila
June 4, 2026
Talla
Kungiyar Hizbullah a yau Alhamis ta yi watsi da yarjejeniyar baya bayan nan da aka cimma tsakanin Isra'ila da gwamnatin Lebanon inda ta bukaci Isra'ila ta janye baki daya daga Lebanon yayin da cigaba da fadan ke kawo tsaiko ga yunkurin kawo karshen yakin Iran.
Sanarwar ta Hizbullah na zuwa ne yayin da wani harin Isra'ila ya kashe mutane hudu a cewar hukumomin yankin. Sannan kuma wani jam'in kiyaye zaman lafiya na Majlisar Dinkin Duniya shi ma ya rasa ransa a musayar wuta da ta ritsa da shi.
Shugaban Hizbullah Naim Kassem a cikin wata sanarwa da aka gabatar ta akwatin talabijin ya baiyana tattaunawar da ake a matsayin abin takaici da tozartarwa.