Matashiya mai saka abin kama kifi
February 9, 2021Talla
Bayan kammala karatunta na boko ne dai, matashiyar ta zabi ta yi wannan sana'ar da za ta dogara da ita wace a cewarta ba sai ta yi aikin gwamnati ba za ta samu dukkan rufin asirin da take bukata. Hadiza Auwal ta bayyana cewa ta samu nasarori a wannan sana'ar, koda yake akwai kalubalen da take fuskanta.
Burin matasa da dama dai, da zaran sun kammala karatunsu su samu aikin gwamnati, sai dai ra'ayin Hadiza ya sha bam-ban da na su. A bisa nasarorin da ta samu a wannan sana'ar, Hadiza ta yi kira ga 'yan uwanta matasa kan muhimancin sana'ar hannu. Masana na ganin, in har matasa za su tashi tsaye su rungumi sana'ar hannu, za'a samu raguwar rashin ayyukan yi da matasan ke fama da shi a Najeriya.