1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaGabas ta Tsakiya

Rikicin Isra'ila da Hezbollah ya dagule

Suleiman Babayo AH
June 3, 2026

Rikicin Gabas ta Tsakiya na kara dagulewa tsakanin Isra'ila da mayakan kungiyar Hezbollah.

https://p.dw.com/p/5EniN
Lebanon Tyros 2026 | Rikicin Gabas ta Tsakiya
Rikicin Gabas ta TsakiyaHoto: AP Photo/picture alliance

Kungiyar Hezbollah  da ke Lebanon ta yi barazanar kai hare-hare biranen Tel Aviv da Haifa na Isra'ila, domin mayar da martani kan hare-haren Isra'ila a kudancin birnin Beirut fadar gwamnatin kasar Lebanon.

Yanayin da ake ciki

Wannan gargadin na zuwa lokacin da Firaminista Benjamin Netanyahu na Isra'ila yake cewa dakarunsa za su kai hare-haren birnin Beirut, muddun kungiyar Hezbollah mai alaka da Iran, ba ta daina kai hare-haren kan Isra'ila ba.

Wani hari na jirage maras amatuka na Isra'ila ya halaka mutane shida a kudancin Lebanon da kuma kudancin birnin Beirut. Lamura suna kara dagulewa tsakanin Isra'ila da kungiyar Hezbollah duk da shiga tsakanin da Amurka ta yi.