SiyasaAfirka
Harin Lakurawa a Kebbin Najeriya ya kashe mutane sama da 30
February 19, 2026
Talla
Harin ta'addanci na kungiyar Lakurawa a wasu kauyukan jihar Kebbi da ke arewacin Najeriya, ya halaka mutane sama da 30, kamar yadda kamfanin dillancin labaran Faransa AFP ya rawaito.
Rundunar 'yan sandan jihar ta bakin mai magana da yawunta Bashir Usman, ta ce lamarin ya faru a ranar Laraba, inda maharan suka lalata kauyuka bakwai, da suka hada da Mamunu da Awasaka da Tungar Tsoho, sai Makangara da Kanzo da Gorun Naidal da kuma Dan Mai Ago.
Karin bayani - Harin ta'addanci a arewacin Najeriya ya halaka mutane 45
Sama da shekaru 16 ke nan da yankin arewacin Najeriya ke fama da hare-haren ta'addanci, daga kungiyoyin masu ikirarin jihadi, wanda ya faro a yankin arewa maso gabashin kasar, har ya fantsama zuwa sauran sassa.