SiyasaGabas ta Tsakiya
Mutane sun mutu a Harin Isra'ila kan Lebanon
April 30, 2026
Talla
Wannan na zuwa ne kusan makonni biyu bayan tsagaita wuta tsakanin Isra'ila da kungiyar Hezbollah.
Sanarwar ma'aikatar lafiyar kasar ta kara da cewa, hare-haren Isra'ilan sun kuma yi sanadiyyar jikkata mutane 23, ciki har da yara takwas da mata bakwai.
An fitar da wannan sanarwa ne jim kadan bayan shugaban Lebanon ya soki abin da ya kira ci gaba da karya yarjejeniyar tsagaita wuta da Isra'ila ke yi.