Najeriya: 'Yan bindiga sun kashe mutane da dama a Filato
February 23, 2026
'Yan bindigar sun kai hare haren ne a yankin Dorawan Babuj da ke karamar hukumar Barikin Ladi, inda suka kashe mutane 9, kafin daga bisani suka shiga kauyen Jol, da ke karamar hukumar Riyom a jihar ta Filato suka kashe mutum guda tare da jikkata wasu da dama.
Karin bayani: Harin ta'addanci na karuwa a Jihar Filato
A wata ganawa da wakilinmu na jihar Filato, Abdullahi Maidawa Kurgwi ya yi da sakataren watsa labarai na kungiyar matasan Berom ta kasa, Wrang Tengwom ya zargin cewar maharan sun kai harin ne a matsayin ramuwar gayya, bayan kisan wasu Fulani biyar a karshen mako. A cewar Kurgwi, ya zuwa yanzu hukumomi a jihar Filato ba su ce komai ba dangane da aukuwar lamarin, sai dai wasu matasa cikin fushi sun toshe babbar hanyar Barkin Ladi, zuwa kudancin jihar Filato don nuna bacin ran su dangane da kashe-kashe da ke aukuwa a yankin.