Haɗarin jirgin ruwa a Tarayyar Najeriya
August 29, 2014Talla
Wani jami'an hukumar ba da agajin gaggawa ta NEMA Onimode Bandele da ya tabbatar da wannan labarin ya shaidawa kamfanin dillancin labarai na AFP cewar suna ta ƙoƙarin ganin sun tsamo sauran mutanen da ba a kai gare su ba.
Mr. Bandele ya ce jirgn ya kife ne bayan da ya tunkuyi wani abu cikin ruwa lokacin da ya ke tafiya. Kifewar jiragen ruwa a Najeriya dai wani abu ne da ake samu daga lokaci zuwa lokaci wanda ake alaƙantawa da yin lodin da ya wuce kima ko gudun wuce sa'a ko ma wata sa'ar rashin ingancin jiragen.
Mawallafi: Ahmed Salisu
Edita: Abdourahamane Hassane