1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaAmurka

Gwamnatin Trump ta yi kiranye ga jakadun kasar 30

December 22, 2025

Gwamnatin Trump ta ce ta dauki wannan mataki domin sauya fasalin diflomasiyyar kasar ta Amurka daidai da zamani.

https://p.dw.com/p/55pdf
Shugaban Amurka Donald Trump
Shugaban Amurka Donald Trump Hoto: Doug Mills/The New York Times/AP Photo/picture alliance

Ma'aikatar Harkokin Wajen Amurka ta ce galibin jakadun sun fara aiki a zamanin tsohuwar gwamnatin Joe Biden. Ma'aikatar ta ce dukkan jakadun da jami'an diflomasiyyar za su dawo birnin Washington DC domin gudanar da wasu ayyukan na daban.

Karin bayani:Sabon matakin diflomasiyyar Trump a Afirka

Kiranyen zai shafi jakadun Amurka a Afirka akalla 13 da suka hadar da na kasashen Burundi, Kamaru, Cape Verde, Gabon, Ivory Coast, Madagascar, Mauritius, Niger, Najeriya, Ruwanda, Senegal, Somalia da kuma Uganda.

Lamarin na zuwa ne a daidai lokacin da dangantaka tsakanin Amurka da wasu kasashe irin su China da Najeriya da Jamhuriyar Nijar da Rasha har ma da Turai ke fuskantar kalubale.