Ko Jonathan zai yi takara a zaben Najeriya?
September 26, 2025
A shekara ta 2015 ne Jonathan ya zamo shugaban kasar na farkon fari da ya karbi kaddamar shan kaye cikin fage na siyasar Najeriya, ya kuma mika mulki ga adawa.
Duk da cewar dai an dade ana ta zawarci na tsoho na shugaban Najeriyar cikin gidan na adawa, wannan ne karo na farkon fari da Goodluck Ebele Jonathan yake nuna alamu na sake komawa cikin fagen na siyasar Najeriya a kai tsaye .
Kuma wata ganawa a tsakaninsa da shugaban jam'iyyar ADC ta adawar David Mark dai yanzu haka na jawo ka ce na ce cikin fagen siyasa da ke dada nuna alamun zafi.
Ana dai kallon tsoho na shugaban da ke da dimbin mabiya a sashensa na kudu maso kudanci na kasar na cikin sahun gaba a masu siyasa ta kasar da ke iya karbar mulki a wurin jam'iyyar APC.
Kokari na kare magana ko kuma bude sabon babi cikin fage na siyasar tarayyar Najeriyar, a baya dai mai dakinsa Patience Jonathan ta ce maigidan nata ya gama da siyasar Najeriyar har abada. Kafin wata nasara ta aboki a Kasar Ghana daga dukka na alamu ta nemi sauya tunani na tsoho na shugaban Najeriyar.
Jonathan da Mahama dai sun sha kaye a a kujera ta shugaban kasar a kasashensu, to sai dai kuma can a kasar Ghanan John Mahama yai nasarar sake karbar mulki – daga hannun jam'iyyar data kada shi ta karbe mulkin.
Ya zuwa yanzun dai tsoho na shugaban ya bi gari yana ta neman afuwar wadanda suke da tunanin ya bata tare da aiyyana yafiya bisa laifin da aka yi masa, a wani abun da ke nuna alamun tunkarar fagen siyasa na kasar a kai tsaye.