1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Gobara ta hallaka mutane a Faransa

Ahmed Salisu
January 12, 2019

Hukumomi a kasar Faransa sun ce mutane biyu sun rasu yayin da wasu da yawansu ya kai 36 suka samu raunuka na kuna sakamakon mummunar gobarar da ta tashi a wani gidan gasa burodi da ke tsakiyar birin Paris.

https://p.dw.com/p/3BS41
Frankreich, Paris: Explosion im 9. Arrondissement
Hoto: Getty Images/AFP/T. Samson

Ministan cikin gidan Faransan Christophe Castaner ya ce biyu daga cikin wadanda suka rasu din ma'aikatan hukumar kashe gobara ne sannan 12 daga cikin mutum 36 da suka jikkata ke cikin matsanancin hali. Babban mai gabatar da kara na birnin na Paris ya ce bayanan da suka samu na nuna cewar gobarar ta tashi ne sakamakon fitar da iskar gas ta rika yi a gidan gasa burodin, lamarin da ya haddasa lalacewar gidan da kuma motoci da ke ajiye a gabansa. Tuni dai hukumomi suka ba da umarnin kwashe mutanen da ke zaune a gidajen da ke kusa inda wannan ibtila'i ya faru don gudun karuwar yawan mutanen da za su jikkata duba da irin yadda wajen ya turnike da hayaki.