1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Faransa na son kungiyar NATO shiga yaki a yankin Sahel

Binta Aliyu Zurmi
November 28, 2019

Shugaba Emmanuel Macron na Faransa ya yi kira ga aminan kasarsa da su shiga yakin da ake yi da mayakan jihadi da ke hana zaman lafiya a yankin Sahel.

https://p.dw.com/p/3TuSD
NATO-Generalsekretär Jens Stoltenberg und Emmanuel Macron
Hoto: NATO

Emmanuel Macron ya fadi hakan ne yayin ganawar da suka yi da shugaban kungiyar tsaro ta NATO Jens Stoltenberg a birnin Paris, inda ya ce yin hakan zai yi matukar tasiri ga dakile ayyukan na ta'addanci. Shugaban na Faransa ya kuma nemi batun ya kasance daya daga cikin manyan batutuwan da kungiyar za ta tattauna a babban taronta da za a gudanar a birnin Landon na Birtaniya nan gaba kadan.