1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Faransa: Kafa gwamnati ce mafita a Libiya

Mouhamadou Awal BalarabeNovember 22, 2015

Gwamnatin Faransa ta hada gwamnatocin biyu na Libiya da su yi wa Allah da ma'aiki da su kafa gwamnatin hadin kan kasa Domin hana kasar fadawa hannun kungiyar IS.

https://p.dw.com/p/1HAJz
Jean-Yves Le Drian
Hoto: AFP/Getty Images/N. Tucat

Wannan shaguben na ministan tsaron Faransa Jean-Yves Le Drian ya biyo bayan wata sanarwa da Libiya ta bayar cewar, kungiyar IS na shirin tattara nata ya nata daga Syriya da niyar kafa tungarta a kasarLibiya. saboda haka ne cikin wata hira da ya yi da tashar rediyo ta Europe1 a birnin Paris, babban jami'in na Faransa ya nemi kasashe makwabta irinsu na Aljeriya da Masar da su kawo dauki don a fitar da Libiya daga halin da ta samu kanta a ciki.

Minista Le Drian ya nunar da cewar masu kaifin kishin addini da Libiya ta kunsa yanzu haka su kai mutane 4000zuwa 5000. A makon da ya gabata a karon farko Amirka ta yi musu ruwan bama-bamai, inda ta yi nasarar kashe Abou Nabil, da ake dangantawa da madagun 'yan Jihadin na Libiya.

Tun bayan hambarar da gwamnatin Moammar kadhafi a shekara ta 2011 ne Libiya ta fada cikin yaki. A yanzu haka dai gwamnatoci biyu na rikicin shugabanci a Libiya daya a Tripoli da kuma daya a Tobruk a gabashi, wacce kasashen duniya suka amince da ita.