1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaAfirka

Turai da Turkiyya na kan hanyar inganta huldarsu

Abdoulaye Mamane Amadou
April 5, 2021

Bayan shafe dogon lokaci suna zaman doya da manja, Kungiyar Tarayyar Turai za ta gabatar wa Turkiyya da sabon jadawalin dawo da huldarsu a ranar Talata mai zuwa.

https://p.dw.com/p/3ragR
Recep Tayyip Erdogan Video Konferenz mit Charles Michel und Ursula von der Leyen
Hoto: Stephanie Lecocq/AP/picture alliance

Shugabar hukumar gudanarwa ta kungiyar EU Ursula von der Leyen da na majalisar Turai Charles Michel, za su yi wata ganawa da Shugaban Turkiyya Recep Tayyip Erdogan a birnin Ankara, domin kara tantance batutuwan da suka shafi huldar bangarorin biyu ciki har da batun tattalin arziki da na 'yan gudun hijira da ke jibge a Turkiyya, kamar yadda taron kolin shuwagabannin kungiyar na ranar 26 ga watan Maris ya gindaya.

Sai dai wannan lamarin na zuwa ne, bayan da kungiyar ta ce ta lura da Shugaba Erdogan ya sassauto daga matsayarsa ta zaman wani shu'umi kan batutuwan da suka shafi kasar Turkiyya da nahiyar Turai.