1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Dubban Mutane sun mutu a Turkiyya da Syria

Abdullahi Tanko Bala
February 6, 2023

Adadin mutanen da suka rasu a girgizar kasar da ta auku a Turkiyya da syria sun haura mutum 2,600 yayin da ma'aikatan agaji ke ci gaba da aikin ceto a kasashen biyu

https://p.dw.com/p/4NAKW
Türkei Diyarbakir Erdbeben
Hoto: Mahmut Bozarslan/AP Photo/picture alliance

Kasashe a fadin duniya na yin gangami domin kai taimakon jinkai da ma'aikatan agaji don aikin ceto a Turkiyya da Syria inda girgizar kasar da ta auku a ranar litinin ta halaka mutane fiye da 2,500

Kasashe a fadin nahiyar Turai da Asiya da Gabas ta Tsakiya da kuma arewacin Amirka sun yi alkawarin kai gudunmawar jinkai.

Kungiyar tarayyar Turai ta aike da tawaga goma ta masu aikin ceto yayin da sakataren Majalisar Dinkin Duniya Antonio Guterres ya yi kira ga kasashe su taimaka wa dubban iyalan da Iftila'in ya ritsa da su wadanda dama can yawancinsu sun dogara ne da tallafi.

Jamus wadda ke da Turkawa miliyan uku da ke zaune a kasar ta yi alkawarin kai agajin gaggawa.

Shugaban Rasha Vladimir Putin ya yi alkawarin kai wa kasashen biyu tallafi a tattaunawar da ya yi ta wayar tarho da shugaban Syria Bashar al Assad da na Turkiyya Recep Tayyip Erdogan.

Shi ma shugaban Ukraine Volodymyr Zelensky ya ce kasarsa wadda yaki daidaita a shirye take ta bada gudunmawa domin shawo kan kalubalen itftila'in.

    

2023-02-06T15:49:50Z UTC