1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Dangote zai zuba jarin dala biliyan daya a Zimbabuwe

Zainab Mohammed Abubakar
November 12, 2025

Dangote zai zuba makuddan kudi wajen bunkasa masana'antu daban daban a Zimbabuwe da ke kudancin Afirka.

https://p.dw.com/p/53Vk5
Aliko Dangote, Geschäftsmann aus Nigeria
Hoto: Christophe Petit Tesson/picture alliance/dpa

Rukunin kamfanonin Dangote na Najeriya zai zuba jarin akalla dalar Amurka biliyan guda a fannin gina bututun mai, da samar da wutar lantarki da kuma masana'antar siminti a Zimbabuwe, in ji jagoran kamfanin Aliko Dangote.

Dangote, wanda ya fi kowa arziki a Afirka, ya gana da shugaban kasar Zimbabuwe Emmerson Mnangagwa, inda bangarorin biyu suka sanya hannu kan yarjejeniyar zuba jari da gwamnati a yau Laraba.

A baya dai hamshakin dan kasuwar ya taba ziyartar Zimbabuwe a shekarar 2015, a zamanin marigayi Shugaba Robert Mugabe wanda Mnangagwa ya gaji kujerarsa bayan juyin mulkin 2017, amma ya yi watsi da shirin zuba jari a kasar da ke kudancin Afirka saboda dalilai marasa tabbas.

Dangote yana da kamfanoni a kasashe 17 na Afirka kuma daya daga cikin rassansu da ke sarrafa siminti na jagorantar dukkan masana'antun yin siminiti na nahiyar.