1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Dandalin Matasa: 05.03.2026

March 12, 2026

A kowace shekara idan aka shiga watan Azumi na Ramadana, da yawa daga cikin matasa na turuwa zuwa shan ruwa a masallatai musamman a garuruwan da ake ware kudi domin ciyar da masu Azumi.

https://p.dw.com/p/5AHFX
Hoto: Afolabi Sotunde/REUTERS

Gwamnatin jihar Sokoto ta ware naira biliyan don aikin ciyarwa a azumin Ramadanan bana 2026, kuma tuni matasa suka fara dandazo a wuraren da ake aikin rabon abincin a ko wace rana. A lokacin da aka fara azumin na bana gwamnan jihar Sokoto Ahmed Aliyu ya yi kira ga masu hannau da shuni a jihar su taimaka wajen cikyar da mabuƙata ganin yadda matasa da dama da kuma gajiyayyu ke amfana da hakan.