1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

CIA ta bankado umarnin kashe Jamal Khashoggi

Zulaiha Abubakar
November 17, 2018

Wata kafar yada labaran Amirka ta ruwaito cewa hukumar CIA ta yi imanin cewa yarima mai jiran gadon Saudiyya shine ya bayar da umarnin kashe dan jaridar nan Jamal Khashoggi

https://p.dw.com/p/38Qwc
Jamal Khashoggi
Hoto: imago/IP3press/A. Morissard

Jami'an hukumar Leken Asirin Amirka sun yanke cewar Yarima Muhammad bin Salman na kasar Saudiyya ne ya bada umarnin a kashe 'dan Jaridar nan Jamal Kashoggi.

Sai dai  babu tabbas ko jakadan Saudiyya a Turkiyya na da masaniya game da shirin aikata kisan kai a karamin ofishin Jakadancin Saudiyan dake Istanbul cikin sakamkon binciken da suka gudanar sai dai gwamnatin Saudiyya ta yi watsi da wannan batu.

A wani sabon labarin kuma Hukumar ta bankado wata hira tsakanin marigayi Kashoggi  da Khalid bin Salman Jakadan Saudiyya a Amirka a wayar tarho inda Jakadan ya ke ba Kashoggi tabbacin tsaron lafiyar sa idan  ya je karbar takardun neman sabon auren da zai yi a karamin Ofishin jakadancin Saudiyyan dake Istanbul .

Masu rajin kare hakkin dan Adam dai na ci gaba da yin Allah wadai da kokarin tsame Yarima Muhammad bin Salman daga zargin kisan dan Jaridar Jamal Kashoggi