1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaAsiya

China ta yanke wa tsoffin ministocin tsaronta hukuncin kisa

Abdulkarim Muhammad Abdulkarim
May 7, 2026

Tsoffin ministocin sun aikata laifin cin hanci da rashawa lokacin da suke aiki tsakanin shekarar 2018 zuwa 2023.

https://p.dw.com/p/5DQeT
Tsoffin ministocin tsaron China Wei Fenghe da Li Shangfu, wadanda aka yankewa hukuncin kisa saboda karbar cin hanci da rashawa
Tsoffin ministocin tsaron China Wei Fenghe da Li Shangfu, wadanda aka yankewa hukuncin kisa saboda karbar cin hanci da rashawaHoto: TASS/dpa/picture alliance

Wata kotun soja a China, ta yanke wa tsoffin ministocin tsaron kasar biyu hukuncin kisa, sakamakon samunsu da aikata laifukan cin hanci da rashawa, kamar yadda kafar yada labaran kasar ta Xinhua ta sanar.

Karin bayani:Firaministan Birtaniya zai kai ziyara Chaina

Tsoffin ministocin sun hada da Wei Fenghe da Li Shangfu, wadanda suka yi aiki tsakanin shekarar 2018 zuwa 2023, inda bayan shekaru biyu, za a mayar da hukuncin zuwa daurin ra-da-rai maimakon kisa, tare da kwace komai da suka mallaka a duniya.

Karin bayani:China ta gudanar da gagarumin atisaye a yankin Taiwan 

Wannan dai wani bangare ne na yaki da cin hanci da rashawa da shugaban China Xi Jinping ya zafafa a kai, wanda ya gano mutanen da karbar na goro, a lokacin da suke rike da mukami.