1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

AU ta yi tir da tsare Shugaba Kabore

Abdul-raheem Hassan
January 24, 2022

Kungiyar Tarayyar Afirka AU, ta yi Allah wadai da yunkurin juyin mulki da sojoji suka yi a Burkina Faso, bayan tsare Shugaba Roch Mach Christian Kabore da ministocinsa ba tare da sanin inda suke ba ko halin da suke ciki.

https://p.dw.com/p/461MK
Moussa Faki, shugaban kungiyar Tarayyar Afirka
Hoto: Michael Kappeler/picture alliance/dpa

A wata sanarwa da Shugaban kungiyar AU Moussa Faki Mahamat ya fitar, ya yi kira ga sojojin Burkina Faso da jami'an tsaro, su tabbatar da

hakkinsu na tsaron kasa tare da kare lafiyar Shugaba Kabore da mambobin gwamnatinsa da suka kama.

Sojojin Burkina Faso sun sanar da tsare Shugaba Kabore da ministocinsa kwana guda bayan da 'yan tawaye suka kwace wani barikin soji, inda suka yi ta artabu da bindigogi a babban birnin kasar da ke yammacin Afirka.

Ba a dai bayyana ko wane ne ke rike da ragamar mulkin kasar ba zuwa yanzu, amma wata sanarwa a shafin Twitter na Shugaba Roch Marc Christian Kabore, ya yi kira ga sojoji da su ajiye makamansu, duk da cewa sojoji sun yi kawanya a kafar yada labaran kasar.