1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Amirka za ta taimaka wa Turkiyya

Ramatu Garba Baba
February 19, 2023

A wannan Lahadin Sakataren Harkokin wajen Amirka Antony Blinken ke ziyara kasar Turkiyya don ganewa idanunsa girman ta'asar da girgizar kasa ta haifar a kudancin kasar.

https://p.dw.com/p/4NhYY
Sakataren Harkokin wajen Amirka Antony Blinken
Sakataren Harkokin wajen Amirka Antony BlinkenHoto: David Josek/REUTERS

A wannan Lahadin Sakataren Harkokin wajen Amirka Antony Blinken ke kai ziyara kasar Turkiyya don ganewa idanunsa girman ta'asar da iftla'in da girgizar kasa ta haifar a yankin kudancin kasar. Ana sa ran babban jami'in zai gana da Shugaba Recep Tayyip Erdogan don tattauna batutuwa da suka shafi taimakon da kasar ke bukata a yanayin da ta tsinci kai.

A ranar shida ga wannan watan na Fabrairu, girgizar kasa mai karfin maki 7.8 a ma'aunin Rista, ta auku a yankin kudancin Turkiyya da arewacin Siriya, kawo yanzu mutum fiye da dubu arba'in da biyar aka tabbatar sun mutu a yayin da wasu fiye da miliyan daya suka rasa matsuguninsu baya ga dubban da ke jinya a asibiti. Masana tattalin arziki na hasashen cewa, kasashen na bukatar biliyoyin dalloli kafin su sake iya gina yankunan da iftala'in ya lalata.