1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Bayern Munich za ta karbi dan wasan Manchester City

May 6, 2020

Kungiyar da ke rike da kambun wasannin kwallon kafar Bundesliga ta Jamus Bayern Munich ta kammala shirin karbar dan wasan kungiyar Manchester City ta Ingila Leroy Sane.

https://p.dw.com/p/3brMt
Corona-Lockerungen in Europa
Hoto: Reuters/A. Gebert

Hakan zai faru ne a karkashin wani tsari na musanya. Leroy Sane dan asalin kasar Jamus ya jima bai taka leda ba tun a watan Agustan da ya gabata bayan da ya samu rauni a gwiwarsa. 

Sai dai rahotanni sun ce har yanzu ba su daddale a kan ko nawa Bayern Munich za ta biya Manchester City a kan wannan musaya ba. Amma dai wasu na cewa ko nawa aka ba Manchester City za ta karba tun da a yanzu tana cikin matsalar rashin kudi saboda annobar coronavirus. 

Wannan musaya dai na zuwa ne yayin da a wannan Laraba gwamnatin Jamus da gwamnoni 16 na jihohin kasar ke ganawa don duba yiwuwar bude wasannin Bundesliga a cikin wannan wata.