An saki matukan jirgin ruwan Turkiyya
February 12, 2021Talla
Illahirin ma'aikatan jirgin dai 'yan asalin kasar Turkiyar ne, sai wani guda dan asalin kasar Azerbaijan wanda barayin suka hallaka.
Jirgin da ya nufi birnin Cape Town na Afirka ta Kudu, an sauya masa akala ne bayan tashinsa da kilomitoci 160 daga birnin Legas na Tarayar Najeriya.
Sai dai babu bayanan hanyoyin da aka bi wajen sakin ma'aikatan, an biya kuddaden fansa ko ko a'a.