An sace wani baturen Sweden a Najeriya
August 9, 2021Talla
Rundunar tsaro ta 'yan sandan jahar Ogun a Najeriya, ta ce, wasu 'yan bindiga sun yi garkuwa da wani bature dan kasar Sweden da kuma wani mutum guda dan Najeriya a jahar ta Ogun da ke Kudancin kasar. Mutum guda ya rasa ransa a yayin musayar wuta a tsakanin 'yan bindigan da tawagar wadanda aka sacen, kafin daga bisani su yi nasarar yin awon gaba da mutanen biyu.
Abimbola Oyeyemi, kakakin rundunar 'yan sandan jahar, ya ce lamarin ya faru ne a yayin da tawagar da ke yiwa baturen rakiya suka ziyarci wata gonar kiwon dabbobi a yammancin ranar Asabar din da ta gabata. Matsalar satar mutane dai don neman kudin fansa na kara yin kamari a Najeriya.