An kwace gidajen tsohuwar ministar mai
February 28, 2018Talla
Diezani Alison-Madueke da ke zama mace ta farko da ta shugabanci kungiyar kasasahe masu fitar da albarkatun mai ta OPEC ta yi aiki karkashin tsohon Shugaba Goodluck Jonathan har zuwa 2015.
Ita dai Mrs. Alison-Madueke na fiskantar tarin tuhume-tuhume na badakalar cin hanci da rashawa a ciki da wajen kasar ta Najeriya ciki kuwa har da a Birtaniya inda a watan Oktoba na 2015 a ka kamata a birnin London bayan da Birtaniya ta kaddamar da binciken kasa da kasa a kanta.