1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An ceto daliban jami'ar Gusau biyar daga hannun 'yan bindiga

Abdoulaye Mamane Amadou
March 17, 2024

Biyar daga cikin daliban jam'ar tarayya ta Gusau a jihar Zamfara na Najeriya sun samu sa'ida, bayan da aka ceto su daga hannun 'yan bindiga.

https://p.dw.com/p/4dpR7
Wasu daliban makarantar bokon Gusau da aka karbo daga hannun 'yan bindiga
Wasu daliban makarantar bokon Gusau da aka karbo daga hannun 'yan bindigaHoto: Sunday Alamba/AP Photo/picture alliance

Gwamnatin jihar Zamfara da ke arewacin Najeriya ta tabbatar da kubutar da dalibai biyar daga cikin 15 da 'yan bindiga suka sace a jami'ar gwamnatin tarayya da ke Gusau a jihar.

Mai magana da yawun gwamnan jihar Mustafa Jafaru Kaura ya shaida wa wakilin DW Yuusf Ibrahim Jargaba cewar akwai wasu karin mutanen da gwamnati ta kubutar tare da daliban guda biyar.

Tun watanni shida da suka gabata ne dai 'yan bindiga suka shiga jami'ar ta Gusau da ake wa lakabi da FUGUS inda suka yi awon gaba da wadannan dalibai mata. Yanzu hankali ya koma kan sauran 'yan mata 10 da ke hannun 'yan bindigar.