Najeriya: Harin yan bindiga ya hallaka jama'a
July 10, 2021Talla
Shedu sun tabbatar wa kamfanin dillancin labarai na AFP da cewa, wadanda suka hallaka sun haura mutun 40, baya ga wasu bakwai da ke kwance a gadon asibiti a yayin hare-haren da 'yan fashin dajin suka kai kan kauyuka biyar na jihar ta Zamfara.
Wanannn lamarin na zuwa ne a yayin da ko a ranar Larabar da tagabata, wasu 'yan fashin daji suka hallaka mutun takwas a kauyen Tsauwa da ke jihar Katsina mai makwaftaka da Zamfara, yankunan da matsalar sace-sacen jama'a da garkuwa da daliban makarantu don neman kudin fansa ke ke kara ta'azzara.