1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaJamus

An kashe dan majalisar dattawa a Kamaru

January 12, 2022

Wasu 'yan bindiga da ke gwagwarmaya da makamai a yankin dake neman ballewa a Kamaru, sun kashe wani dan majalisa. Dan majaliosar da aka kashe dai dan adawa ne.

https://p.dw.com/p/45Run
Kamerun Beerdigung des achtjährigen Nsoh Macpeace in Bamenda
Hoto: Adrian Kriesch/DW

An halaka wani dan majalisa a birnin Bamenda da ke arewa maso yammacin Jamhuriyar Kamaru, yankin da ke fama da rikicin 'yan aware masu fafutikar kafa kasa.

An gano gawar dan majalisar mai suna Henry Kemende ne bayan zargin wasu 'yan bindiga da ba a kai ga tantance su ba da halaka shi a ranar Talata.

Shi dai marigayin dan majalisar na Kamaru, dan jam'iyyar nan ta Social Democratic Front ne da ke hamayya.

Mataimakin shugaban jam'iyyar SDF,  Joshua Osih, ya ce sun karbi gawar dan majalisar dauke da harbin bindiga a jiki.

Ya zuwa yanzu babu wani ko wasu da suka dauki alhakin kisan dan majalisar na Kamaru.