1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Najeriya: 'Yan matan da aka sace a Neja sun tsere

Abdoulaye Mamane Amadou
November 23, 2025

A daidai lokacin da wasu 50 daga cikin 'yan matan makarantar Saint Mary na jihar Neja suka kubuta, gwamnatin Najeriya ta sanar da ceto masu ibada 38 daga hannun 'yan bindiga.

https://p.dw.com/p/545Ar
Takalmin wasu dalibai 'yan makaranta da aka sace a Najeriya
Takalmin wasu dalibai 'yan makaranta da aka sace a NajeriyaHoto: KOLA SULAIMON/AFP

Jami'an tsaron Najeriya sun ceto wasu mutane 38 mabiya addinin Kirista da aka yi garkuwa da su a wani harin na ranar Talatar da tagabata, a daidai lokacin da suke tsaka da ibada a kauyen Eruku na jihar Kwara.

Shugaba Bola Ahmed Tinubu, ya sanar a wani sakon da ya fitar a ranar Lahadi, yana mai cewa tare "da taimakon jami'an tsaronmu, daukacin masu ibadar da aka sace daga cocin Eruku na jihar Kwara sun kubuta". Duk da yake shugaban bai yi wani karin haske ba.

'Yan matan da ake yi garkuwa da su sun kubuta

Dalibai 50 daga cikin fiye da 300 da aka sace a makarantar nan ta Katolika da ke jihar Neja sun tsere daga hannun masu garkuwa da su, in ji kungiyar CAN ta Kiristocin Najeriya, amma kungiyar,  ba ta yi wani karin haske kan ragowar daliban ba da malamansu 12 da hadarin ya rutsa da su ba. 

Wane hali iyayen dalibai ke ciki a Kebbi?

Dakunan kwana na dalibai 'yan makaranta da aka sace a Najeriya
Dakunan kwana na dalibai 'yan makaranta da aka sace a NajeriyaHoto: Christian Association of Nigeria/AP Photo/picture alliance

Wasu masu dauke da makamai da har yanzu ba a tabbatar da ko su wane ne ba, suka kai hari a sanyin safiyar ranar Juma’a a makarantar St. Mary's Catholic School da ke jihar Neja, tare da sace daliban fiye da 300, satar da ke zaman irinta mafi muni a tarihin kasar, tun bayan sace 'yan matan Chibok shekaru 10 da suka gabata. 

Ba wata kungiya da ta yi ikrarin kai harin tare da sace 'yan mata

Har yanzu ba wata kungiyar da ta fito ta dauki alhakin kai harin na jihar Neja, ko kuwa harin Maga na jihar Kebbi a yankin arewa maso yammacin Najeriya.

Jagoran mabiya darikar Katolika Léon na 14 ya yi kira da a ceto daliban da aka yi garkuwa da su, tare da nuna kaduwarsa game da sace-sacen malaman addnini da dalibai a kasashen Najeriya da Kamaru.

'Yan bindiga sun sace 'yan makaranta 25 a Najeriya

Shugaban Amurka Donalnd Trump, da ya yi barazanar kai wa 'yan ta'adda hari don ceto Kiristocin Najeriya, ya bayyana abin da ke faruwa a Najeriya amatsayin abin kunya.