1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Ceto bakin-haure a Libiya

Suleiman Babayo
July 12, 2019

Masu gadin tekun Libiya sun kama jirgin ruwa dauke da bakin-haure fiye da 20

https://p.dw.com/p/3M0V3
Libyen Luftangriff Tajoura Detention Center bei Tripolis
Hoto: Reuters/I. Zitouny


Masu gadin gabar tekun Libiya sun bayyana kama wani jirgin ruwa dauke da bakin-haure fiye da 20 masu neman tsallaka teku domin shiga kasashen Turai. Kofofin yada labaran kasar ta Libiya sun ce bakin-haure sun fito daga kasashen Masar, da Sudan, gami da Libiya.

A cikin wata sanarwa hukumomin sun bayyana mika mutane ga masu aikin jinkai gami da taimakon lafiya, inda aka kai su wani sasansanin 'yan gudun hijira.