1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Amnesty ta kalubalanci kame mata a Imo

August 24, 2018

Kungiyar kare hakkin dan Adam ta Amnesty International, ta nemi hukumomin Najeriya su gaggauta sako mata 114 da aka tsare bayan zanga-zangar neman sakin jagoran IPOB Nnamdi Kanu.

https://p.dw.com/p/33hg7
Amnesty international Logo
Hoto: picture-alliance/dpa/S.Kahnert

Wani alkali a birnin Oweri na jihar Imo, ya nemi ci gaba da tsare matan da aka kame a lokacin zanga-zanagar har zuwa watan Satumba mai zuwa. Sai dai kungiyar Amnesty International na ganin matakin a matsayin wuce gona da iri kamar yadda kakin kungiyar a Najeriya Isa Sunusi ya sheda wa DW: "Kundin tsarin mulki ya ba wa kowa 'yancin fadin albarkacin bakinsa, muna kira da a gaggauta sako su, tun da dai ba su tayar da hankalin kowa ba."

Demonstration für politischen Aktivisten Nwannekaenyi Nnamdi Kenny Okwu Kanu
Hoto: Getty Images/AFP/P.U. Ekpei

Kame sama da mata 100 da aka yi, na zuwa ne kasa da 'yan sa'o'i da wani zaben kananan hukumomi a jihar Imo, wannan ya sa ake danganta zanga-zangar da siyasa. Kungiyar IPOB ta jima tana fafutukar neman rajin ballewa daga Najerya domin kafa tata kasa mai cin gashin kanta, abin da ya haifar da fargaba da neman haddasa rarrabuwar kawuna a kasar a lokutan baya. Gwamnatin Najeriya ta haramta ayyukan kungiyar tare da ayyana ta a matsayin kungiyar 'yan ta'adda.