1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Amnesty: Rikicin makiyaya ya halaka mutum fiye da 3,600

Ramatu Garba Baba
December 17, 2018

Kungiyar kare hakkin dan Adam ta Amnesty International, ta ce akalla mutum fiye da 3,600 ne suka mutu a sanadiyar rikicin manoma da makiyaya da aka samu a sassan Najeriya daga shekarar 2016.

https://p.dw.com/p/3AE8u
Logo von Amnesty International

Rahoton da kungiyar ta fitar a wannan Litinin ya nunar cewa wadannan mutanen sun mutu ne a rikicin da ya auku tun daga shekarar 2016, sai dai ta ce an fi samun asarar rayuka daga rikice rikicen da suka auku a cikin wannan shekarar.

Rahoton ya ci gaba da cewa, rashin daukar mataki na gudanar da sahihin bincike tare da hukunta wadanda aka samu da laifi, na daga cikin dalilan da ke assasa rikici a sassan Najeriya. Masana a nasu bangaren, sun baiyana fargabar barkewar sabon rikici a yayin da ake shirin shiga yanayin rani ganin a wannan lokacin ne makiyaya suke soma yawo da dabbobinsu don samar musu abinci.