'Yan Najeriya akalla 600 za a mayar gida
September 9, 2019Talla
Jakadan Najeriya a Afrika ta Kudu Godwin Adamu ne ya sanar ma kamfanin dillancin Labaran Faransa AFP matakin da gwamnatin kasar ta dauka, na kwashe mutum akalla dari shida (600) a wannan makon. Jirgin farko na kamfanin Air Peace, zai tashi ne a ranar Laraba da mutum dari uku da shirin (320) injin jakadan.
Rikicin kin jinin baki da Afrika ta Kudu ta yi kaurin suna a kai, ya kara kamari inda 'yan Najeriya suka kasance mafi yawa daga cikin wadanda lamarin ya shafa asarar rayuka da dukiya a hargitsin na baya-bayan nan. Wasu 'yan Najeriya sun mayar da martani tare da lalata kamfanoni mallakin Afrika ta Kudun da ke a sassan kasar.