1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaAfirka

Najeriya ta fitar da sunayen 'yan wasanta na gasar AFCON

December 26, 2021

Hukumar NFF ta sanar da jerin 'yan kwallo 28 da za su buga mata wasan AFCON a Kamaru, ciki har da Ahmed Musa da Kenneth Omeruo wadanda ke cikin 'yan wasan kasar a shekara ta 2013, lokacin da Najeriya ta lashe gasar. 

https://p.dw.com/p/44qRk
Fußball Nigeria gegen Elfenbeinküste
Hoto: CAF

Hukumar Kwallon Kafar Najeriya, NFF ta sanya dan wasa Victor Osimhen, dan kasar da ke buga wa kungiyar Napoli ta Italiya a cikin 'yan wasan da za su kare mata mutunci a fafatawar da za a yi da ita a gasar kwallon kafar Afirka ta AFCON. 

Victor Osimhen na cikin hutunsa na watanni uku a Napoli ne bayan wani rauni da ya samu a watan Nuwamba a fuskarsa. Amma tun a farkon makon nan aka gan shi yana atisaye, sannan ya wallafa cewa yana fatar zai shiga cikin 'yan wasan da za su buga wa Najeriya a gasar ta AFCON wace ake sa ran gudanarwa a watan gobe na Janairu a kasar Kamaru.