1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Kalubalan rayuwar mata zawarawa a kasar Hausa

Zulaiha Abubakar GAT
August 27, 2019

A kasar Hausa, matan da ke rayuwar zawarci bayan rasa aurensu a bisa dalili na mutuwar aure ko mutuwar miji na fuskantar a wasu lokuttan kalubalai na tsangwaman da ma zargi daga danginsu da sauran al'umma.

https://p.dw.com/p/3OYEW
Nigeria Frauen erzählen vor ihre Gefangenschaft bei Boko Haram
Hoto: Reuters

Sakamakon yadda wasu daga cikin matan da aurensu ya mutu ke fuskantar kunci daga irin kallon da al'umma ke yi musu ciki kuwa har da mata 'yan uwansu, da dangi da kawaye, idan ba an yi dace da iyaye ko 'yan uwa masu sassauci da rungumar kaddara ba, macen da aurenta ya mutu ta kan shiga wani yanayi na rana zafi inuwa kuna.