1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Aljeriya ta nuna fargabar sake shiga yakin basasa

Mahmud Yaya Azare
March 1, 2019

Masu zanga-zanga a Aljeriya suna kara samun goyon baya kan nuna adawa da matakin Shugaba Abdel-Aziz Bouteflika na sake neman sabon wa'adin mulki karo na biyar.

https://p.dw.com/p/3EJXr
Algerien Proteste gegen die Regierung
Hoto: picture-alliance/AP Photo/F. Gudoum

Jam'iyyun adawa da kungiyoyin masu fafutika a kasar Aljeriya sun jagorancir zanga-zangar gama gari a kasar, don nuna adawa da sake tsayawar takarar shugaban kasar, Abdel-Aziz Bouteflika, karo na biyar, babban hafsan sojin kasar ya yi gargadin jefa kasar cikin yakin basasa, makamancin wanda aka taba yi a kasar a shekarar 1991.

Algerien - Studentenproteste
Hoto: picture-alliance/F. Batiche

Jami'o'i da dalibansu sun amsa kiran zanga-zangar gama garin dake adawa da matakin tazarce karo na biyar da shugaba Butifilikan key i karo na biyar ke nan, wasunsu suka dauke da akwatunan daukar gawa da ke alamta sallar gawa ga mulkin Bouteflika, zanga-zangar da sannu-sannu take rikidewa  zuwa ta neman sauyi.

Ita kungiyar 'yan jaridar kasar, dama  kananan ma'aikatan da ke aiki a kafofin watsa labaran gwamnati, sun bi sahun masu zanga-zangar, suna masu alwashin bayyana wa 'yan kasa gaskiyar abin da ke wakana.

Algerien - Studentenproteste
Hoto: picture-alliance/F. Batiche

Tuni dai gamayyar jam'iyun adawa a kasar, suka fara wani kudirin doka da zai takaita wa'adin mulki a kasar, duk kuwa da cewa, sun sai zai yi wuya majalisar da jam'iyya mai mulki ke da rinjaye ta amince da kudurin.

Idan dai ana iya tunawa, a shekarar 1991 ne sojojin kasar ta Aljeriya, suka soke zaben da masu kishin Islama suka lashe, lamarin da yakai ga barkewar yakin basasa da yakai ga halaka dubun-dubatan 'yan kasar.