Za a yi wa sojoji shari'a kan kisan gilla
June 24, 2019Talla
Mai magana da yawun ma'aikatar Cyrille Serge, ya ce za a gurfanar dasu don amsa tambayoyi kan zargin hada baki wajen aikata kisan gilla tare da cin amanar kasa. A bara ne aka yi ta watsa hoton bidiyo a kafofin sada zumunta na zamani, da ya nuna wasu da kayan sojoji suna harbe mata da yara. Lamarin da ya sa gwamnatin Kamaru kaddamar da bincike kan sahihancin bidiyon.