Za a gudanar da bincike kan rikicin Gaza
July 23, 2014Talla
Wannan dai ya biyo bayan korafin da Falasdinu ta gabatar gaban hukumar mai mambobi 46, inda 29 daga cikin mambobin da suka hada da kasashen Larabawa da Rasha da China da kasashen Latin Amirka da na nahiyar Afirka sun amince da gudanar da binciken.
To sai dai Amirka ta kada kuri'ar kin amince da kudurin yayin da kasahen Turai galibinsu na kungiyar EU suka yi rowar kuri'unsu. Wannan dai na zuwa ne daidai lokacin da kasashen duniya ke cigaba da neman ganin an kawo karshen zub da jinin da ake yi.
Mawallafi: Ahmed Salisu
Edita: Zainab Mohammed Abubakar