1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Kotun ICC za ta fara shari'ar tsohon shugaban Philippines

Zainab Mohammed Abubakar
January 26, 2026

Cikin watann Febrairu ne tsohon shugaban Philippines Rodrigo Duterte zai gurfana a gaban a kotun ICC da ke Hague.

https://p.dw.com/p/57U8J
Philippinen Manila 2024 | Ex-Präsident Rodrigo Duterte vor Senatsausschuss zu Anti-Drogen-Krieg
Hoto: Aaron Favila/AP Photo/picture alliance

Alkalan kotun hukunta manyan laifuka na ICC da ke birnin Hague, sun  yanke hukuncin cewar, watan Febrairu ne tsohon shugaban Philippines Rodrigo Duterte zai gurfana agaban a kotun, tare da watsi da hujjojin cewa mai shekaru 80 din ba shi karfin fuskantar shari'a.

A ranar 23 ga Fabrairu ne dai Duterte zai fuskanci shari'ar tabbatar  da tuhume-tuhumen da ke kan shi, inda alkalai za su yanke hukunci ko zarge-zargen masu gabatar da kara sun isa hujjar ci gaba da shari'a a kansa.

Masu gabatar da kara na ICC sun tuhumi Duterte da laifuka uku na cin zarafin bil'adama, suna zarginsa da hannu a kisan kai 76 a matsayin wani bangare na yakinsa da miyagun kwayoyi.