Ba a da tabbbas dangane zaɓen wanda ke cike da ruɗani
July 21, 2015Talla
'Yan adawar ƙasar sun ce zaɓen bai halarta ba,saboda takarar shugaba Pierre Nkuriziza a waadi na uku, ta saɓama kudin tsarin mulkin ƙasar.
Tun da farko Cocin Roman Katolika na ƙasar ta janye daga lura da saka ido a kan al'amuran zaɓen saboda rashin sahihancinsa.
A jiya a cikin dare an ji ƙaran wasu abubuwan da suka fashe tare da jin ɗuriyar harbe-harbe wanda aka ci gaba da yin harbe-harben.Wasu rahotannin da ke zo mana sun ce mutane biyu sun mutu ɗaya ɗan sanda da wani farar hula.