1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Ba a da tabbbas dangane zaɓen wanda ke cike da ruɗani

Abdourahamane HassaneJuly 21, 2015

An buɗe runfuna zaɓe a Burundi a zaɓen shugaban ƙasar da ke gudana a yau cikin rikici.Wanda'yan adawar suka ƙaurace masa kann cewar za saɓama doka.

https://p.dw.com/p/1G1wB
Parlamentswahlen in Burundi
Hoto: AFP/Getty Images/L. Nshimiye

'Yan adawar ƙasar sun ce zaɓen bai halarta ba,saboda takarar shugaba Pierre Nkuriziza a waadi na uku, ta saɓama kudin tsarin mulkin ƙasar.

Tun da farko Cocin Roman Katolika na ƙasar ta janye daga lura da saka ido a kan al'amuran zaɓen saboda rashin sahihancinsa.

A jiya a cikin dare an ji ƙaran wasu abubuwan da suka fashe tare da jin ɗuriyar harbe-harbe wanda aka ci gaba da yin harbe-harben.Wasu rahotannin da ke zo mana sun ce mutane biyu sun mutu ɗaya ɗan sanda da wani farar hula.