1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaAfirka

Iran da Amirka: Farfado da yarjejeniyar nukiliya

Abdoulaye Mamane Amadou
April 6, 2021

Amirka a karon farko karkashin jagorancin gwamnatin Joe Biden za ta halarci wani taron tattaunawa kan yiwuwar ceto yarjejeniyar nukiliyar Iran.

https://p.dw.com/p/3rbw7
Iran Urananreicherungsanlage in Natanz
Hoto: AEOI/ZUMA Wire/imago images

Masu aiko da rahotanni sun ce Iran da Amirkar ba za su hadu kai tsaye a yayin tattaunawar ba, to amma tawagogin kasashen Turai ne za su kasance masu shiga tsakani a yunkurinsu na sake dawo da yarjejeniyar, wacce tsohon shugaban Amirka Donald Trump ya yi fatali da ita a baya.

Daukacin manyan kasashen duniya da suka rattaba hannu kan yarjejeniyar ta Viennan dai irin su Jamus Faransa da Birtaniya da Rasha da China za su halarci wani taron, a yayin da a share daya wasu kwarru daga Amirkar za su gabatar da nasu taron amma ba tare da Iran ba.